< Zabura 57 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Ten compasión de mí, oh ʼElohim. Ten compasión de mí. Porque mi alma confía en Ti, Y en la sombra de tus alas me amparo Hasta que pase la destrucción.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Clamaré a ʼElohim ʼElyón, A ʼEL, Quien me favorece.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Él enviará desde el cielo Y me salvará de la infamia del que me oprime. (Selah) ʼElohim enviará su misericordia y su verdad.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Mi vida está en medio de leones. Estoy tendido entre los que respiran fuego. Hijos de hombres, sus dientes son lanzas y flechas, Y su lengua, espada aguda.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
¡Exaltado seas sobre los cielos, oh ʼElohim! ¡Tu gloria sea sobre toda la tierra!
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Tendieron una red ante mis pies para doblegar mi vida. Cavaron un hoyo delante de mí Y ellos cayeron en él. (Selah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Mi corazón está establecido, oh ʼElohim. Está firme mi corazón. Cantaré y entonaré salmos.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Despierta, alma mía. Despierten, arpa y lira. Yo despertaré el alba.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Te daré gracias entre los pueblos, oh ʼAdonay. Te cantaré salmos en las naciones.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Porque tu misericordia es grande hasta los cielos, Y tu verdad, hasta las nubes.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Exaltado seas sobre los cielos, oh ʼElohim. Y tu gloria sea por encima de toda la tierra.