< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Para o músico chefe. Ao som da música “Não Destruir”. Um poema de David, quando ele fugiu de Saul, na caverna. Tenha misericórdia de mim, Deus, tenha misericórdia de mim, pois minha alma se refugia em você. Sim, na sombra de suas asas, eu me refugiarei, até que o desastre tenha passado.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Eu clamo a Deus Altíssimo, a Deus que atende aos meus pedidos por mim.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Ele enviará do céu, e me salvará, ele repreende aquele que me persegue. (Selah) Deus enviará sua bondade amorosa e sua verdade.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Minha alma está entre os leões. Eu estou entre aqueles que são incendiados, mesmo os filhos dos homens, cujos dentes são lanças e flechas, e sua língua uma espada afiada.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Seja exaltado, Deus, acima dos céus! Que sua glória esteja acima de toda a terra!
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Eles prepararam uma rede para meus passos. Minha alma está curvada. Eles cavam um buraco diante de mim. Eles próprios caem no meio dela. (Selah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Meu coração está firme, Deus. Meu coração está firme. Cantarei, sim, cantarei louvores.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Wake acima, minha glória! Acorde, alaúde e harpa! Vou acordar o amanhecer.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Eu te darei graças, Senhor, entre os povos. Cantarei louvores a vocês entre as nações.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Pois sua grande bondade amorosa chega até os céus, e sua verdade para os céus.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Seja exaltado, Deus, acima dos céus. Que sua glória esteja sobre toda a terra.

< Zabura 57 >