< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
MAING Kot, kom kotin maki ong ia, maki ong ia! Pwe ngen i kin kaporoporeki komui, o pan mot en lim omui i wasan ai maur, lao ansau apwal daulier.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
I likwir ong Kot, me lapalapia, ong Kot, me kotin kaimwisokala ai kankangeranger.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
A kotin poronedo sang nanlang sauas pa i ong me kanamenok ia, o me kin ngiringir ong ia. (Sela) Kot pan kotin kadarado a kalangan o melel.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Ngen i mi nan pung en laien akan, aramas rasong umpul en kisiniai; ngi arail rasong katieu o kanangan kasik katieu, o lo arail rasong kodlas kong o.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Maing Kot, kom kotida ileila sang lang, o wau omui nan sappa karos.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Irail insarai ia nan al ai kan; re kin katoutoui ngen i; re weirada mo i por eu, ap pein pupedi ong lole. (Sela)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Mongiong i insenemaular, Maing Kot, ngen i onoper ong kaul o kaping.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Ngen i pirida! Kaul o arp pirida! I pan pirida nin soran.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Ieowa, i men danke ong komui nan wei kan; i pan kauli ong komui nan pung en aramas akan.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Pwe omui kalangan me laud dueta nanlang, o omui melel dueta tapok kan.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Maing Kot, kom kotida ileila sang lang, o wau omui lingan nan sappa karos.

< Zabura 57 >