< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
برای رهبر سرایندگان: در مایۀ «نابود نکن». غزل داوود دربارۀ زمانی که داوود از چنگ شائول به غار گریخت. ای خدا بر من رحم کن! بر من رحم کن، زیرا به تو پناه آورده‌ام. در زیر سایۀ بالهایت پناه می‌گیرم تا این بلا از من بگذرد.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
نزد خدای متعال، خدایی که همهٔ نیازهایم را برمی‌آورد، دعا می‌کنم.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
او از آسمان دعای مرا شنیده، مرا نجات خواهد بخشید و دشمنم را شکست خواهد داد. خدا محبت و وفاداری خود را از من دریغ نخواهد داشت.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
مردم درنده‌خو مانند شیر مرا محاصره کرده‌اند. دندانهای آنها همچون نیزه و پیکان و زبانشان مانند شمشیر، تیز و برّان است.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
ای خدا، جلال و شکوه تو بالاتر از آسمانها قرار گیرد و عظمت تو بر تمام جهان آشکار شود.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
دشمنانم برایم دام گسترده‌اند تا مرا گرفتار سازند و من در زیر بار غصه خم شده‌ام. آنها در سر راه من چاه کندند، اما خودشان در آن افتادند.
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
ای خدا، من روحیهٔ خود را نباخته‌ام و اعتماد خود را از دست نداده‌ام. من سرود خواهم خواند و تو را ستایش خواهم کرد.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
ای جان من بیدار شو! ای بربط و عود من، به صدا درآیید تا سپیده دم را بیدار سازیم!
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
خدایا، در میان مردم تو را سپاس خواهم گفت و در میان قومها تو را ستایش خواهم کرد،
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
زیرا محبت تو بی‌نهایت عظیم است.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
ای خدا، جلال و شکوه تو بالاتر از آسمانها قرار گیرد و عظمت تو بر تمام جهان آشکار شود.

< Zabura 57 >