< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Mictam di Davide, intorno a ciò ch'egli se ne fuggì nella spelonca, d'innanzi a Saulle; [dato] al Capo de' Musici, [sopra] Al-tashet ABBI pietà di me, o Dio; abbi pietà di me; Perciocchè l'anima mia si confida in te, Ed io ho la mia speranza nell'ombra delle tue ale, Finchè sieno passate le calamità.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Io griderò all'Iddio altissimo; A Dio che dà compimento a' fatti miei.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Egli manderà dal cielo a salvarmi; Egli renderà confuso colui ch'è dietro a me a gola aperta. (Sela) Iddio manderà la sua benignità, e la sua verità.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
L'anima mia [è] in mezzo a' leoni; Io giaccio [fra] uomini incendiari, I cui denti [son] lance, e saette, E la cui lingua [è] spada acuta.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Innalzati, o Dio, sopra i cieli; [Innalzisi] la tua gloria sopra tutta la terra.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Essi avevano apparecchiata una rete a' miei passi, [Già] tiravano a basso l'anima mia; Avevano cavata una fossa davanti a me; [Ma] essi vi sono caduti dentro. (Sela)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Il mio cuore è disposto, o Dio; il mio cuore è disposto; Io canterò, e salmeggerò.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Gloria mia, destati; destati, saltero, e cetera; Io mi risveglierò all'alba.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Io ti celebrerò, o Signore, fra i popoli; Io ti salmeggerò fra le nazioni;
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Perciocchè la tua benignità [è] grande infino al cielo, E la tua verità infino alle nuvole.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Innalzati, o Dio, sopra i cieli; [Innalzisi] la tua gloria sopra tutta la terra.

< Zabura 57 >