< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Mictam de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Al-tasheth: touchant ce qu'il s'enfuit de devant Saül en la caverne. Aie pitié de moi; ô Dieu! Aie pitié de moi; car mon âme se retire vers toi, et je me retire sous l'ombre de tes ailes, jusqu'à ce que les calamités soient passées.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Je crierai au Dieu souverain, au [Dieu] Fort, qui accomplit [son œuvre] pour moi.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Il enverra des cieux, et me délivrera; il rendra honteux celui qui me veut dévorer; (Sélah) Dieu enverra sa gratuité et sa vérité.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Mon âme est parmi des lions; je demeure parmi des boutefeux; parmi des hommes dont les dents sont des hallebardes et des flèches, et dont la langue est une épée aiguë.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Ô Dieu! élève-toi sur les cieux, [et] que ta gloire soit sur toute la terre.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Ils avaient préparé le rets à mes pas; mon âme penchait [déjà]. Ils avaient creusé une fosse devant moi, mais ils sont tombés au milieu d'elle; (Sélah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Mon cœur est disposé, ô Dieu! mon cœur est disposé, je chanterai et psalmodierai.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Réveille-toi ma gloire, réveille-toi musette et violon, je me réveillerai à l'aube du jour.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Seigneur, je te célébrerai parmi les peuples, je te psalmodierai parmi les nations.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Car ta gratuité est grande jusqu'aux cieux, et ta vérité jusqu'aux nues.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Ô Dieu! élève-toi sur les cieux, [et] que ta gloire soit sur toute la terre!

< Zabura 57 >