< Zabura 57 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Au chef de musique. Al-Tashkheth. De David. Mictam; quand il fuyait devant Saül, dans la caverne. Use de grâce envers moi, ô Dieu! use de grâce envers moi; car en toi mon âme se réfugie, et sous l’ombre de tes ailes je me réfugie, jusqu’à ce que les calamités soient passées.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Je crierai au Dieu Très-haut, à Dieu qui mène [tout] à bonne fin pour moi.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Il a envoyé des cieux, et m’a sauvé; il a couvert de honte celui qui veut m’engloutir. (Sélah) Dieu a envoyé sa bonté et sa vérité.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Mon âme est au milieu de lions; je suis couché parmi ceux qui soufflent des flammes, – les fils des hommes, dont les dents sont des lances et des flèches, et la langue une épée aiguë.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Élève-toi, ô Dieu! au-dessus des cieux; que ta gloire soit au-dessus de toute la terre!
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Ils ont préparé un filet pour mes pas, mon âme se courbait; ils ont creusé devant moi une fosse, ils sont tombés dedans. (Sélah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Mon cœur est affermi, ô Dieu! mon cœur est affermi; je chanterai et je psalmodierai.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Éveille-toi, mon âme! Éveillez-vous, luth et harpe! Je m’éveillerai à l’aube du jour.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Je te célébrerai parmi les peuples, ô Seigneur! je chanterai tes louanges parmi les peuplades;
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Car ta bonté est grande jusqu’aux cieux, et ta vérité jusqu’aux nues.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Élève-toi, ô Dieu! au-dessus des cieux; que ta gloire soit au-dessus de toute la terre!