< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Pour le chef musicien. Sur l'air de « Do Not Destroy ». Un poème de David, quand il fuyait Saül, dans la grotte. Soyez miséricordieux envers moi, Dieu, soyez miséricordieux envers moi, car mon âme se réfugie en toi. Oui, à l'ombre de tes ailes, je me réfugie, jusqu'à ce que le désastre soit passé.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Je crie vers le Dieu Très Haut, à Dieu qui accomplit mes demandes pour moi.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Il enverra du ciel, et me sauvera, il réprimande celui qui me poursuit. (Selah) Dieu enverra sa bonté et sa vérité.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Mon âme est parmi les lions. Je me trouve parmi ceux qui sont incendiés, même les fils des hommes, dont les dents sont des lances et des flèches, et leur langue une épée tranchante.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Sois exalté, Dieu, au-dessus des cieux! Que ta gloire soit au-dessus de toute la terre!
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Ils ont préparé un filet pour mes pas. Mon âme s'est inclinée. Ils creusent une fosse devant moi. Ils tombent eux-mêmes au milieu de tout ça. (Selah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Mon cœur est inébranlable, Dieu. Mon cœur est inébranlable. Je vais chanter, oui, je vais chanter des louanges.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Réveille-toi, ma gloire! Réveille-toi, luth et harpe! Je vais réveiller l'aube.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Je te louerai, Seigneur, parmi les peuples. Je chanterai tes louanges parmi les nations.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Car ta grande bonté atteint les cieux, et votre vérité dans les cieux.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Sois exalté, Dieu, au-dessus des cieux. Que ta gloire soit sur toute la terre.

< Zabura 57 >