< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
Davidin kultainen kappale, edelläveisaajalle, ettei hän hukkunut, kuin hän Saulin edestä pakeni luolaan. Jumala, ole minulle armollinen, ole minulle armollinen; sillä sinuun minun sieluni uskaltaa, ja sinun siipeis varjon alle minä turvaan siihenasti, että ahdistukset ohitse käyvät.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
Minä huudan korkeimman Jumalan tykö, sen Jumalan tykö, joka minun vaivani päälle lopun tekee.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
Hän lähettää taivaasta, ja varjelee minua, ja antaa ne häpiään tulla, jotka minua tahtovat niellä ylös, (Sela) lähettäköön Jumala armonsa ja totuutensa.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
Minun sieluni makaa jalopeurain keskellä, jotka ovat niinkuin tulen liekki; ihmisten lapset, joiden hampaat ovat keihäs ja nuolet, ja heidän kielensä terävä miekka.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Korota itses, Jumala, taivasten ylitse ja sinun kunnias ylitse kaiken maan.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
Verkon he virittivät minun käymiseni eteen, ja minun sieluni vältti: kuopan he kaivoivat minun eteeni, ja siihen he itse lankesivat, (Sela)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
Valmis on sydämeni, Jumala, valmis on sydämeni veisaamaan ja kiittämään.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Herää kunniani, herää psaltari ja kantele, varhain minä tahdon herätä.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Herra, sinua minä tahdon kiittää kansain seassa, ja veisata pakanain seassa.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
Sillä sinun armos on suuri hamaan taivaisiin asti, ja sinun totuutes pilviin asti.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Korota itses, Jumala, taivasten ylitse, ja sinun kunnias ylitse kaiken maan.

< Zabura 57 >