< Zabura 57 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
God, be merciful to me! Act mercifully toward me because I come to you to protect me. I ask you to protect me [like little birds are protected under their mother’s] wings [MET] until the storm/danger is ended.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
God, you who are greater than all other gods, I cry out to you, the one who enables me to do all that you desire.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
You will answer me from heaven and rescue me, but you will cause those who oppress me to be [defeated and] disgraced! (Think about that!) God will [always] faithfully love me and (will be faithful/will do what he promises).
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
[Sometimes] I am surrounded by [my enemies who are like] lions that [kill] humans; [they are like] lions that chew with their teeth [animals that they kill]; but my enemies have spears and arrows, not teeth; and [the false things that] they say [MTY] [hurt people as much as] sharp swords [hurt people] [MET].
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
God, show in the heavens that you are very great! And show your glory to people all over the earth!
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
[It is as if] [MET, HYP] my enemies spread a net to seize me, and I became very distressed [IDM]. [It is as if] [MET, HYP] they dug a deep pit along the path where I walk, but they themselves fell into it!
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
God, I have complete confidence [DOU] in you. I will sing to you, and I will praise you while I sing.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
I will awaken myself; I will arise before the sun rises and [praise you while I play] my harp or my (lyre/small harp).
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
Lord, I will thank you among [all] the people; and I will sing to praise you among [many] ethnic groups,
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
because your faithful love for us is [as great as the distance from the earth] to the sky, and because your (faithfulness/faithfully doing what you promise) is [as great as the distance] up to the clouds [MET].
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
God, show in the heavens that you are very great! And show your glory [to people] all over the earth!

< Zabura 57 >