< Zabura 56 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
Til sangmesteren; efter "Den målløse due på de fjerne steder"; av David; en gyllen sang da filistrene grep ham i Gat. Vær mig nådig, Gud! for mennesker vil opsluke mig; hele dagen trenger de mig med krig.
2 Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
Mine fiender søker å opsluke mig hele dagen; for mange er de som strider mot mig i overmot.
3 Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
På den dag jeg frykter, setter jeg min lit til dig.
4 Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
Ved Gud priser jeg hans ord; til Gud setter jeg min lit, jeg frykter ikke; hvad skulde kjød kunne gjøre mig?
5 Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
Hele dagen forvender de mine ord; alle deres tanker er mig imot til det onde.
6 Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
De slår sig sammen, de lurer, de tar vare på mine trin, fordi de står mig efter livet.
7 Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
Skulde de undslippe tross sin ondskap? Støt folkeslag ned i vrede, Gud!
8 Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
Hvor ofte jeg har flyktet, det har du tellet; mine tårer er gjemt i din flaske; står de ikke i din bok?
9 Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
Da skal mine fiender vende tilbake, på den dag jeg roper; dette vet jeg at Gud er med mig.
10 Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
Ved Gud priser jeg ordet; ved Herren priser jeg ordet.
11 ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
Til Gud setter jeg min lit, jeg frykter ikke; hvad skulde et menneske kunne gjøre mig?
12 Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
På mig, Gud, hviler løfter til dig; jeg vil betale dig med takksigelser.
13 Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
For du har fridd min sjel fra døden, ja mine føtter fra fall, så jeg kan vandre for Guds åsyn i de levendes lys.

< Zabura 56 >