< Zabura 56 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
For the Chief Musician. To the tune of “Silent Dove in Distant Lands.” A poem by David, when the Philistines seized him in Gath. Be merciful to me, God, for man wants to swallow me up. All day long, he attacks and oppresses me.
2 Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
My enemies want to swallow me up all day long, for they are many who fight proudly against me.
3 Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
When I am afraid, I will put my trust in you.
4 Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
In God, I praise his word. In God, I put my trust. I will not be afraid. What can flesh do to me?
5 Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
All day long they twist my words. All their thoughts are against me for evil.
6 Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
They conspire and lurk, watching my steps. They are eager to take my life.
7 Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
Shall they escape by iniquity? In anger cast down the peoples, God.
8 Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
You count my wanderings. You put my tears into your container. Aren’t they in your book?
9 Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
Then my enemies shall turn back in the day that I call. I know this: that God is for me.
10 Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
In God, I will praise his word. In the LORD, I will praise his word.
11 ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
I have put my trust in God. I will not be afraid. What can man do to me?
12 Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
Your vows are on me, God. I will give thank offerings to you.
13 Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
For you have delivered my soul from death, and prevented my feet from falling, that I may walk before God in the light of the living.

< Zabura 56 >