< Zabura 56 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
Be merciful to me, O God, for man would swallow me up. Fighting all the day long he oppresses me.
2 Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
My enemies would swallow me up all the day long, for they are many who fight proudly against me.
3 Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
What time I am afraid, I will put my trust in thee.
4 Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
In God I will praise his word. In God I have put my trust. I will not be afraid. What can flesh do to me?
5 Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
All the day long they wrest my words. All their thoughts are against me for evil.
6 Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
They gather themselves together. They hide themselves. They mark my steps, even as they have waited for my soul.
7 Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
Shall they escape by iniquity? In anger cast down the peoples, O God.
8 Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
Thou number my wanderings. Put thou my tears into thy bottle. Are they not in thy book?
9 Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
Then shall my enemies turn back in the day that I call. This I know, that God is for me.
10 Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
In God I will praise his word. In Jehovah I will praise his word.
11 ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
In God I have put my trust. I will not be afraid. What can man do to me?
12 Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
Thy vows are upon me, O God. I will render thank offerings to thee.
13 Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
For thou have delivered my soul from death, and my feet from falling, that I may walk before God in the light of the living.

< Zabura 56 >