< Zabura 56 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
達味金詩,交與樂官。 天主,求你憐憫我,因為人要謀害我,時時處處有人欺壓我。
2 Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
我的仇敵終日謀害我,攻擊我的人實在眾多。
3 Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
至高者!恐惶侵襲我的時日,我只有全心仰賴你。
4 Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
我全心倚賴天主,並歌頌祂的許諾;我決不怕血肉的人,對我要做什麼。
5 Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
他們終日破壞我的生活,千方百計地想加害於我;
6 Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
他們群集埋伏,窺伺我的行徑,他們等待時機,謀圖我的性命。
7 Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
天主,求你審判他們的罪行;求你在盛怒中將異民敉平。
8 Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
我多次流離失所,你都知悉,我的眼淚聚在你皮囊裏;豈不是也寫在你的書卷內?
9 Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
我幾時呼號你,我的仇敵便退卻,從此我也全知道,天主常扶助我。
10 Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
我全心倚賴天主,歌頌祂的許諾;
11 ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
決不怕脆弱的人,對我要做什麼。
12 Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
天主,我必遵守向你所許的願,我必要向你償還頌謝的祭獻。
13 Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
因為你救我脫離死亡,使我的腳免於跌仆,使我能在活人的光明中,在天主的面前行走。

< Zabura 56 >