< Zabura 55 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Pazljivo prisluhni moji molitvi, oh Bog in ne skrij se pred mojo ponižno prošnjo.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Prisluhni mi in me usliši. V svoji pritožbi žalujem in zganjam hrup
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
zaradi glasu sovražnika, zaradi zatiranja zlobnega, kajti name mečejo krivičnost in z besom me sovražijo.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Moje srce znotraj mene je boleče zaskrbljeno in strahote smrti so padle name.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Strah in trepet sta prišla name in groza me je preplavila.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Rekel sem: »Oh da bi imel peruti kakor golobica! Kajti potem bi odletel proč in bi bil miren.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Glej, potem bi odtaval daleč proč in ostal v divjini. (Sela)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
Pospešil bi svoj pobeg pred vetrovnim viharjem in neurjem.«
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Uniči, oh Gospod in razdeli njihove jezike, kajti videl sem nasilje in prepir v mestu.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Dan in noč hodijo okrog po njegovih zidovih. Tudi vragolija in bridkost sta v njegovi sredi.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Zlobnost je v njegovi sredi. Prevara in zvijača ne odideta iz njegovih ulic.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Kajti ni bil sovražnik, ki me je grajal, potem bi to lahko prenesel. Niti ni bil, kdor me je sovražil, ki se je poveličal zoper mene, potem bi se skril pred njim.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Toda bil si ti, človek, moj vrstnik, moj vodnik in moj znanec.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Skupaj sva imela prijetno namero in družno hodila v Božjo hišo.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
Naj se jih polasti smrt in naj hitro gredo dol v pekel, kajti zlobnost je v njihovih bivališčih in med njimi. (Sheol )
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Kar se mene tiče, bom klical k Bogu in Gospod me bo rešil.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Zvečer, zjutraj in opoldan bom molil in glasno vpil. Slišal bo moj glas.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
V miru je osvobodil mojo dušo pred bitko, ki je bila zoper mene, kajti mnogo jih je bilo z menoj.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Bog bo slišal in jih prizadel, celó on, ki ostaja od davnine. (Sela) Ker nimajo sprememb, zato se ne bojijo Boga.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Svoje roke je iztegnil zoper tiste, ki so v miru z njim; prelomil je svojo zavezo.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
Besede iz njegovih ust so bile bolj gladke kakor maslo, toda v njegovem srcu je bila vojna. Njegove besede so bile mehkejše kakor olje, čeprav so bile izvlečeni meči.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Svoje breme vrzi na Gospoda in on te bo podpiral. Nikoli ne bo dopustil, da bi bil pravični omajan.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Toda ti, oh Bog, jih boš zrušil v jamo uničenja. Krvoločni in varljivi ljudje ne bodo preživeli polovice svojih dni, jaz pa bom zaupal vate.