< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
В конец, в песнех разума, Асафу, псалом. Внуши, Боже, молитву мою и не презри моления моего:
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
вонми ми и услыши мя: возскорбех печалию моею, и смятохся
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
от гласа вражия и от стужения грешнича: яко уклониша на мя беззаконие и во гневе враждоваху ми.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Сердце мое смятеся во мне, и боязнь смерти нападе на мя:
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
страх и трепет прииде на мя, и покры мя тма.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
И рех: кто даст ми криле яко голубине? И полещу, и почию.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Се, удалихся бегая и водворихся в пустыни.
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
Чаях Бога спасающаго мя от малодушия и от бури.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Потопи, Господи, и раздели языки их: яко видех беззаконие и пререкание во граде.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Днем и нощию обыдет и по стенам его: беззаконие и труд посреде его, и неправда:
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
и не оскуде от стогн его лихва и лесть.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Яко аще бы враг поносил ми, претерпел бых убо: и аще бы ненавидяй мя на мя велеречевал, укрылбыхся от него.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Ты же, человече равнодушне, владыко мой и знаемый мой,
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
иже купно наслаждался еси со мною брашен: в дому Божии ходихом единомышлением.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
Да приидет же смерть на ня, и да снидут во ад живи: яко лукавство в жилищих их, посреде их. (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Аз к Богу воззвах, и Господь услыша мя.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Вечер и заутра и полудне повем и возвещу, и услышит глас мой.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Избавит миром душу мою от приближающихся мне: яко во мнозе бяху со мною.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Услышит Бог, и смирит я сый прежде век: несть бо им изменения, яко не убояшася Бога.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Простре руку свою на воздаяние: оскверниша завет Его.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
Разделишася от гнева лица Его, и приближишася сердца их: умякнуша словеса их паче елеа, и та суть стрелы.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Возверзи на Господа печаль твою, и Той тя препитает: не даст в век молвы праведнику.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Ты же, Боже, низведеши их в студенец истления: мужие кровей и льсти не преполовят дний своих. Аз же, Господи, уповаю на Тя.

< Zabura 55 >