< Zabura 55 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Inclina ó Deus os teus ouvidos à minha oração, e não te escondas da minha súplica.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Atende-me, e ouve-me: lamento na minha queixa, e faço ruído,
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
Pelo clamor do inimigo e por causa da opressão do ímpio: pois lançou sobre mim a iniquidade, e com furor me aborrecem.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
O meu coração está dolorido dentro de mim, e terrores da morte cairam sobre mim.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Temor e tremor vieram sobre mim; e o horror me cobriu.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Pelo que disse: Oh! quem me dera asas como de pomba! porque então voaria, e estaria em descanço.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Eis que fugiria para longe, e pernoitaria no deserto (Selah)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
Apressar-me-ia a escapar da fúria do vento e da tempestade.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Despedaça, Senhor, e divide as suas línguas, pois tenho visto violência e contenda na cidade.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
De dia e de noite a cercam sobre os seus muros; iniquidade e malícia estão no meio dela.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Maldade há dentro dela: astúcia e engano não se apartam das suas ruas.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Pois não era um inimigo que me afrontava: então eu o houvera suportado: nem era o que me aborrecia que se engrandecia contra mim, porque dele me teria escondido.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Mas eras tu, homem meu igual, meu guia e meu intimo amigo.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Consultávamos juntos suavemente, e andavamos em companhia na casa de Deus.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
A morte os assalte, e vivos desçam ao inferno; porque há maldade nas suas habitações e no meio deles. (Sheol )
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Porém eu invocarei a Deus, e o Senhor me salvará.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
De tarde e de manhã e ao meio dia orarei; e clamarei, e ele ouvirá a minha voz.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Livrou em paz a minha alma da peleja que havia contra mim; pois havia muitos comigo.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Deus ouvirá, e os afligirá, aquele que preside desde a antiguidade (Selah) porque não há neles nenhuma mudança, e portanto não temem a Deus
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Ele pôs as suas mãos naqueles que tem paz com ele: quebrou a sua aliança.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
As palavras da sua boca eram mais macias do que a manteiga, mas havia guerra no seu coração: as suas palavras eram mais brandas do que o azeite: contudo, eram espadas nuas.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Lança a tua carga sobre o Senhor, e ele te susterá: não permitirá nunca que o justo seja abalado.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Mas tu, ó Deus, os farás descer ao poço da perdição; homens de sangue e de fraude não viverão metade dos seus dias; mas eu em ti confiarei.