< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Inclina ó Deus os teus ouvidos á minha oração, e não te escondas da minha supplica.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Attende-me, e ouve-me: lamento na minha queixa, e faço ruido,
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
Pelo clamor do inimigo e por causa da oppressão do impio: pois lançou sobre mim a iniquidade, e com furor me aborrecem.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
O meu coração está dolorido dentro de mim, e terrores da morte cairam sobre mim.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Temor e tremor vieram sobre mim; e o horror me cobriu.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Pelo que disse: Oh! quem me déra azas como de pomba! porque então voaria, e estaria em descanço.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Eis que fugiria para longe, e pernoitaria no deserto (Selah)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
Apressar-me-hia a escapar da furia do vento e da tempestade.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Despedaça, Senhor, e divide as suas linguas, pois tenho visto violencia e contenda na cidade.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
De dia e de noite a cercam sobre os seus muros; iniquidade e malicia estão no meio d'ella.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Maldade ha dentro d'ella: astucia e engano não se apartam das suas ruas.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Pois não era um inimigo que me affrontava: então eu o houvera supportado: nem era o que me aborrecia que se engrandecia contra mim, porque d'elle me teria escondido.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Mas eras tu, homem meu egual, meu guia e meu intimo amigo.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Consultavamos juntos suavemente, e andavamos em companhia na casa de Deus.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
A morte os assalte, e vivos desçam ao inferno; porque ha maldade nas suas habitações e no meio d'elles. (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Porém eu invocarei a Deus, e o Senhor me salvará.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
De tarde e de manhã e ao meio dia orarei; e clamarei, e elle ouvirá a minha voz.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Livrou em paz a minha alma da peleja que havia contra mim; pois havia muitos comigo.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Deus ouvirá, e os affligirá, Aquelle que preside desde a antiguidade (Selah) porque não ha n'elles nenhuma mudança, e portanto não temem a Deus
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Elle poz as suas mãos n'aquelles que teem paz com elle: quebrou a sua alliança.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
As palavras da sua bocca eram mais macias do que a manteiga, mas havia guerra no seu coração: as suas palavras eram mais brandas do que o azeite: comtudo, eram espadas nuas.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Lança a tua carga sobre o Senhor, e elle te susterá: não permittirá nunca que o justo seja abalado.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Mas tu, ó Deus, os farás descer ao poço da perdição; homens de sangue e de fraude não viverão metade dos seus dias; mas eu em ti confiarei.

< Zabura 55 >