< Zabura 55 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Kumqondisi wokuhlabela. Kutshaywa iziginci. Ihubo likaDavida. Lalela umkhuleko wami, Oh Nkulunkulu, ungafulatheli isikhalazo sami;
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
ngizwa ungiphendule. Imicabango yami iyangikhathaza, ngididekile
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
ngelizwi lesitha sami, lokunyonkolozwa ngababi; ngoba bangibangela inhlupho bangithuka bethukuthele.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Inhliziyo yami iyatshiseka ngaphakathi kwami; ukwesaba ukufa kuyangiqinela.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Ukwesaba lokuthuthumela sekungihlasele; isithuli sesingigabhela.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Ngathi, “He, aluba ngangilamaphiko njengejuba! Ngangizaphapha ngizoziphumulela kude.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Ngangizabaleka ngiye kude ngiyehlala enkangala;
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
ngangizaphanga ngiye enqabeni yami, kude kwesikhukhula lesiphepho.”
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Sanganisa ababi, Oh Thixo, sanganisa ukukhuluma kwabo, ngoba ngibona udlakela lengxabano edolobheni.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Emini lebusuku bayacathama emidulini yalo; umona lenzondo kugcwele lapho.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Imimoya yokubhidliza yiyo esibusa; izisongo lamanga akusasuki emigwaqweni.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Aluba ngithukwa yisitha ngingakubhensela lokho; aluba ongizondayo engivukela ngingamcatshela.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Kodwa nguwe, umuntu njengami, umkhula wami, umngane wami oseduze,
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
engake ngaba lobudlelwano obukhulu laye lapho sasihamba ndawonye labanengi endlini kaNkulunkulu.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
Yekela ukufa kuzijume izitha zami; yekela bagqitshelwe bephila engcwabeni, ngoba ububi buthe khoxo phakathi kwabo. (Sheol )
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Kodwa ngiyambiza uNkulunkulu, uThixo angisindise.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Kusihlwa, ekuseni lemini ngiyakhala ngisosizini, yena uyalizwa ilizwi lami.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Uyangihlenga ngingakalimali kuleyompi engihlaselayo, loba bebanengi abaxabana lami.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
UNkulunkulu osesihlalweni sobukhosi lanininini, uzabezwa abachithachithe abantu abangaguqukiyo ezindleleni zabo njalo abangamesabiyo uNkulunkulu.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Umkhula wami uyabahlasela abangane bakhe; wephula isivumelwano asenzayo.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
Inkulumo yakhe ibutshelezi njengolaza, kodwa kulempi enhliziyweni yakhe amazwi akhe alolozela ukwedlula amafutha kodwa abukhali kulensingo.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Yethula inswelo zakho kuThixo yena uzakusekela; akazukuyekela abalungileyo bawe.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Kodwa wena, Nkulunkulu ababi uzabawisela egodini lokungcola; abantu abomele igazi njalo abakhohlisayo kabasoze bayiphile ingxenye yezinsuku zabo. Kodwa mina, ngithemba kuwe.