< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
神よねがはくは耳をわが祈にかたぶけたまへ わが懇求をさけて身をかくしたまふなかれ
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
われに聖意をとめ 我にこたへたまへ われ歎息によりてやすからず悲みうめくなり
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
これ仇のこゑと惡きものの暴虐とのゆゑなり そはかれら不義をわれに負せ いきどほりて我におひせまるなり
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
わが心わがうちに憂ひいたみ死のもろもろの恐懼わがうへにおちたり
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
おそれと戰慄とわれにのぞみ甚だしき恐懼われをおほへり
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
われ云ねがはくは鴿のごとく羽翼のあらんことを さらば我とびさりて平安をえん
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
みよ我はるかにのがれさりて野にすまん (セラ)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
われ速かにのがれて暴風と狂風とをはなれん
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
われ都のうちに強暴とあらそひとをみたり 主よねがはくは彼等をほろぼしたまへ かれらの舌をわかれしめたまへ
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
彼等はひるもよるも石垣のうへをあるきて邑をめぐる 邑のうちには邪曲とあしき企圖とあり
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
また惡きこと邑のうちにあり しへたげと欺詐とはその街衢をはなるることなし
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
われを謗れるものは仇たりしものにあらず もし然りしならば尚しのばれしなるべし 我にむかひて己をたかくせし者はわれを恨たりしものにあらず若しかりしならば身をかくして彼をさけしなるべし
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
されどこれ汝なり われとおなじきもの わが友われと親しきものなり
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
われら互にしたしき語らひをなし また會衆のなかに在てともに神の家にのぼりたりき
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
死は忽然かれらにのぞみ その生るままにて陰府にくだらんことを そは惡事その住處にありその中にあればなり (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
されど我はただ神をよばんヱホバわれを救ひたまふべし
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
夕にあしたに晝にわれなげき且かなしみうめかん ヱホバわが聲をききたまふべし
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
ヱホバは我をせむる戰闘よりわが霊魂をあがなひいだして平安をえしめたまへり そはわれを攻るもの多かりければなり
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
太古よりいます者なる神はわが聲をききてかれらを惱めたまべし (セラ) かれらには變ることなく神をおそるることなし
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
かの人はおのれと睦みをりしものに手をのべてその契約をけがしたり
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
その口はなめらかにして乳酥のごとくなれどもその心はたたかひなり その言はあぶらに勝りてやはらかなれどもぬきたる劍にことならず
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
なんぢの荷をヱホバにゆだねよさらば汝をささへたまはん ただしき人のうごかさるることを常にゆるしたまふまじ
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
かくて神よなんぢはかれらを亡の坑におとしいれたまはん血をながすものと詭計おほきものとは生ておのが日の半にもいたらざるべし 然はあれどわれは汝によりたのまん

< Zabura 55 >