< Zabura 55 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Per il Capo de’ musici. Per strumenti a corda. Cantico di Davide. Porgi orecchio alla mia preghiera o Dio, e non rifiutar di udir la mia supplicazione.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Attendi a me, e rispondimi; io non ho requie nel mio lamento, e gemo,
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
per la voce del nemico, per l’oppressione dell’empio; poiché mi gettano addosso delle iniquità e mi perseguitano con furore.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Il mio cuore spasima dentro di me e spaventi mortali mi son caduti addosso.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Paura e tremito m’hanno assalito, e il terrore mi ha sopraffatto;
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
onde ho detto: Oh avess’io delle ali come la colomba! Me ne volerei via, e troverei riposo.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Ecco, me ne fuggirei lontano, andrei a dimorar nel deserto; (Sela)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
m’affretterei a ripararmi dal vento impetuoso e dalla tempesta.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Annienta, Signore, dividi le loro lingue, poiché io vedo violenza e rissa nella città.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Giorno e notte essi fanno la ronda sulle sue mura; dentro di essa sono iniquità e vessazioni.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Malvagità è in mezzo a lei, violenza e frode non si dipartono dalle sue piazze.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Poiché non è stato un nemico che mi ha fatto vituperio; altrimenti, l’avrei comportato; non è stato uno che m’odiasse a levarmisi contro; altrimenti, mi sarei nascosto da lui;
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
ma sei stato tu, l’uomo ch’io stimavo come mio pari, il mio compagno e il mio intimo amico.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Insieme avevamo dolci colloqui, insieme ce n’andavamo tra la folla alla casa di Dio.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
Li sorprenda la morte! Scendano vivi nel soggiorno de’ morti! poiché nelle lor dimore e dentro di loro non v’è che malvagità. (Sheol )
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Quanto a me: io griderò, a Dio e l’Eterno mi salverà.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
La sera, la mattina e sul mezzodì mi lamenterò e gemerò, ed egli udrà la mia voce.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Egli darà pace all’anima mia, riscuotendola dall’assalto che m’è dato, perché sono in molti contro di me.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Iddio udirà e li umilierà, egli che siede sul trono ab antico; (Sela) poiché in essi non v’è mutamento, e non temono Iddio.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Il nemico ha steso la mano contro quelli ch’erano in pace con lui, ha violato il patto concluso.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
La sua bocca è più dolce del burro, ma nel cuore ha la guerra; le sue parole son più morbide dell’olio, ma sono spade sguainate.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Getta sull’Eterno il tuo peso, ed egli ti sosterrà; egli non permetterà mai che il giusto sia smosso.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Ma tu, o Dio, farai cader costoro nel profondo della fossa; gli uomini di sangue e di frode non arriveranno alla metà de’ lor giorni; ma io confiderò in te.