< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
למנצח בנגינת משכיל לדוד האזינה אלהים תפלתי ואל תתעלם מתחנתי׃
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
הקשיבה לי וענני אריד בשיחי ואהימה׃
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
מקול אויב מפני עקת רשע כי ימיטו עלי און ובאף ישטמוני׃
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
לבי יחיל בקרבי ואימות מות נפלו עלי׃
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
יראה ורעד יבא בי ותכסני פלצות׃
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
ואמר מי יתן לי אבר כיונה אעופה ואשכנה׃
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
הנה ארחיק נדד אלין במדבר סלה׃
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
אחישה מפלט לי מרוח סעה מסער׃
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
בלע אדני פלג לשונם כי ראיתי חמס וריב בעיר׃
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
יומם ולילה יסובבה על חומתיה ואון ועמל בקרבה׃
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
הוות בקרבה ולא ימיש מרחבה תך ומרמה׃
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
כי לא אויב יחרפני ואשא לא משנאי עלי הגדיל ואסתר ממנו׃
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
ואתה אנוש כערכי אלופי ומידעי׃
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
אשר יחדו נמתיק סוד בבית אלהים נהלך ברגש׃
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
ישימות עלימו ירדו שאול חיים כי רעות במגורם בקרבם׃ (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
אני אל אלהים אקרא ויהוה יושיעני׃
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
ערב ובקר וצהרים אשיחה ואהמה וישמע קולי׃
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
פדה בשלום נפשי מקרב לי כי ברבים היו עמדי׃
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
ישמע אל ויענם וישב קדם סלה אשר אין חליפות למו ולא יראו אלהים׃
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
שלח ידיו בשלמיו חלל בריתו׃
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
חלקו מחמאת פיו וקרב לבו רכו דבריו משמן והמה פתחות׃
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
השלך על יהוה יהבך והוא יכלכלך לא יתן לעולם מוט לצדיק׃
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
ואתה אלהים תורדם לבאר שחת אנשי דמים ומרמה לא יחצו ימיהם ואני אבטח בך׃

< Zabura 55 >