< Zabura 55 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Pour la fin, dans les cantiques, intelligence à David. Exaucez, ô Dieu, ma prière, et ne méprisez pas ma supplication.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Portez votre attention sur moi, et exaucez-moi. J’ai été contristé dans ma méditation: et j’ai été troublé
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
À la voix d’un ennemi et à cause de l’oppression du pécheur. Parce qu’ils ont détourné sur moi des iniquités; et par colère ils me tourmentaient.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Mon cœur a été troublé au dedans de moi; et la frayeur de la mort est tombée sur moi.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Une crainte et un tremblement sont venus sur moi; et des ténèbres m’ont couvert.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Et j’ai dit: Qui me donnera des ailes comme les ailes d’une colombe, et je m’envolerai, et je me reposerai?
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Voilà que je me suis éloigné en fuyant: et j’ai demeuré dans le désert.
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
J’attendais celui qui m’a sauvé d’un abattement d’esprit et d’une tempête.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Précipitez- les, Seigneur, divisez leurs langues; parce que j’ai vu l’iniquité et la discorde dans la cité.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Jour et nuit l’iniquité l’environnera sur ses murs: le travail est au milieu d’elle,
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Ainsi que l’injustice. L’usure n’a pas fait défaut dans ses places publiques, ni la fraude.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Car si c’eût été mon ennemi qui m’eût maudit, je l’aurais supporté certainement. Et si celui qui me haïssait avait parlé contre moi avec hauteur, je me serais, sans doute, caché de lui.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Mais c’est toi, homme qui vivais avec moi dans un même esprit, mon guide et mon familier,
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Qui partageais avec moi les doux mets de ma table; nous avons marché dans la maison du Seigneur avec un parfait accord.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol )
Vienne la mort sur eux; et qu’ils descendent dans l’enfer tout vivants: Parce que la méchanceté est dans leurs demeures, au milieu d’eux. (Sheol )
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Mais moi, j’ai crié vers Dieu, et le Seigneur me sauvera.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Le soir, et le matin, et à midi, je raconterai et j’annoncerai ses miséricordes, et il exaucera ma voix.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Il rachètera en paix mon âme de ceux qui s’approchaient de moi; car ils étaient en grand nombre avec moi.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Dieu m’ exaucera, et les humiliera, lui qui est avant les siècles. Car il n’y a pas de changement en eux, et ils n’ont pas craint Dieu.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Il a étendu sa main en leur rendant selon leurs mérites. Ils ont souillé son alliance,
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
Ils ont été dissipés par la colère de son visage; et son cœur s’est approché contre eux.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Déposez vos soins dans le sein du Seigneur, et lui-même vous nourrira; il ne laissera pas éternellement le juste dans l’agitation.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Mais vous, ô Dieu, vous les conduirez dans un puits de destruction. Les hommes de sang et trompeurs n’arriveront pas à la moitié de leurs jours: mais moi, j’espérerai en vous, Seigneur.