< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
Pour le musicien en chef. Sur les instruments à cordes. Une contemplation de David. Écoute ma prière, Dieu. Ne te cache pas de ma supplication.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Occupe-toi de moi, et réponds-moi. Je suis agité dans ma plainte, et gémir
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
à cause de la voix de l'ennemi, à cause de l'oppression des méchants. Car ils me font souffrir. En colère, ils m'en veulent.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
Mon cœur est gravement blessé au-dedans de moi. Les terreurs de la mort se sont abattues sur moi.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
La crainte et le tremblement me saisissent. L'horreur m'a submergé.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
Je disais: « Oh, si j'avais des ailes comme une colombe! Puis je m'envolerais, et je serais en paix.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Voici, je m'égarerais au loin. Je voudrais me loger dans le désert. (Selah)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
« Je me précipiterais vers un abri pour me protéger du vent et de la tempête. »
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Embrouillez-les, Seigneur, et confondez leur langage, car j'ai vu de la violence et des querelles dans la ville.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Jour et nuit, ils rôdent sur ses murs. La malice et l'abus sont également en elle.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Les forces destructrices sont en elle. Les menaces et les mensonges ne quittent pas ses rues.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Car ce n'est pas un ennemi qui m'a insulté, alors j'aurais pu l'endurer. Ce n'est pas non plus celui qui me haïssait qui s'est élevé contre moi, alors je me serais caché de lui.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
Mais c'était toi, un homme comme moi, mon compagnon, et mon ami familier.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Nous avons pris une douce communion ensemble. Nous avons marché dans la maison de Dieu avec de la compagnie.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
Que la mort vienne soudainement sur eux. Qu'ils descendent vivants dans le séjour des morts. Car la méchanceté est au milieu d'eux, dans leur demeure. (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
Quant à moi, j'invoquerai Dieu. Yahvé me sauvera.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Le soir, le matin et à midi, je crierai ma détresse. Il entendra ma voix.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
Il a racheté mon âme en paix de la bataille qui était contre moi, bien qu'il y ait beaucoup de gens qui s'opposent à moi.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
Dieu, qui est sur le trône pour toujours, les entendra et leur répondra. (Selah) Ils ne changent jamais et ne craignent pas Dieu.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Il lève ses mains contre ses amis. Il a violé son alliance.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
Sa bouche était lisse comme du beurre, mais son cœur était la guerre. Ses mots étaient plus doux que de l'huile, mais ce sont des épées dégainées.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Dépose ton fardeau sur Yahvé et il te soutiendra. Il ne permettra jamais aux justes d'être déplacés.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Mais toi, Dieu, tu les feras descendre dans la fosse de la destruction. Les hommes sanguinaires et fourbes ne vivront pas la moitié de leurs jours, mais j'ai confiance en toi.

< Zabura 55 >