< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
For the Chief Musician. On stringed instruments. A contemplation by David. Listen to my prayer, God. Don’t hide yourself from my supplication.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Attend to me, and answer me. I am restless in my complaint, and moan
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
because of the voice of the enemy, because of the oppression of the wicked. For they bring suffering on me. In anger they hold a grudge against me.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
My heart is severely pained within me. The terrors of death have fallen on me.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Fearfulness and trembling have come on me. Horror has overwhelmed me.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
I said, “Oh that I had wings like a dove! Then I would fly away, and be at rest.
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Behold, then I would wander far off. I would lodge in the wilderness.” (Selah)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
“I would hurry to a shelter from the stormy wind and storm.”
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Confuse them, Lord, and confound their language, for I have seen violence and strife in the city.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
Day and night they prowl around on its walls. Malice and abuse are also within her.
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Destructive forces are within her. Threats and lies don’t depart from her streets.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
For it was not an enemy who insulted me, then I could have endured it. Neither was it he who hated me who raised himself up against me, then I would have hidden myself from him.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
But it was you, a man like me, my companion, and my familiar friend.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
We took sweet fellowship together. We walked in God’s house with company.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
Let death come suddenly on them. Let them go down alive into Sheol. For wickedness is among them, in their dwelling. (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
As for me, I will call on God. The LORD will save me.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Evening, morning, and at noon, I will cry out in distress. He will hear my voice.
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
He has redeemed my soul in peace from the battle that was against me, although there are many who oppose me.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
God, who is enthroned forever, will hear and answer them. (Selah) They never change and don’t fear God.
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
He raises his hands against his friends. He has violated his covenant.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
His mouth was smooth as butter, but his heart was war. His words were softer than oil, yet they were drawn swords.
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Cast your burden on the LORD and he will sustain you. He will never allow the righteous to be moved.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
But you, God, will bring them down into the pit of destruction. Bloodthirsty and deceitful men shall not live out half their days, but I will trust in you.

< Zabura 55 >