< Zabura 55 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
TO THE OVERSEER. WITH STRINGED INSTRUMENTS. AN INSTRUCTION OF DAVID. Give ear, O God, [to] my prayer, And do not hide from my supplication.
2 ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
Attend to me, and answer me, I mourn in my (meditation) and make a noise,
3 hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
Because of the voice of an enemy, Because of the oppression of the wicked, For they cause sorrow to move against me, And in anger they hate me.
4 Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
My heart is pained within me, And terrors of death have fallen on me.
5 Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
Fear and trembling come to me, And horror covers me.
6 Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
And I say, “Who gives to me a pinion as a dove?” I fly away and rest,
7 da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
Behold, I move far off, I lodge in a wilderness. (Selah)
8 da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
I hurry escape for myself, From a rushing wind, from a whirlwind.
9 Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
Swallow up, O Lord, divide their tongue, For I saw violence and strife in a city.
10 Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
By day and by night they go around it, on its walls. Both iniquity and perverseness [are] in its midst,
11 Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
Mischiefs [are] in its midst. Fraud and deceit do not depart from its street.
12 Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
For an enemy does not reproach me, or I bear [it], He who is hating me Has not magnified himself against me, Or I hide from him.
13 Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
But you, a man—as my equal, My familiar friend, and my acquaintance.
14 wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
When together we sweeten counsel, We walk into the house of God in company.
15 Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
Desolations [are] on them, They go down [to] Sheol—alive, For wickedness [is] in their dwelling, in their midst. (Sheol h7585)
16 Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
I call to God, and YHWH saves me.
17 Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
Evening, and morning, and noon, I meditate, and make a noise, and He hears my voice,
18 Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
He has ransomed my soul in peace From him who is near to me, For with the multitude they were with me.
19 Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
God hears and afflicts them, And He sits of old. (Selah) Because they have no changes, and do not fear God,
20 Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
He has sent forth his hands against his well-wishers, He has defiled his covenant.
21 Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
His mouth has been sweeter than honey, And his heart [is] war! His words have been softer than oil, And they [are] drawn [swords].
22 Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
Cast on YHWH that which He has given you, And He sustains you, He does not permit the moving of the righteous forever.
23 Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
And You, O God, bring them down To a pit of destruction, Men of blood and deceit do not reach to half their days, And I trust in You!

< Zabura 55 >