< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
Müzik şefi için - Telli sazlarla Davut'un Maskili Zifliler gelip Saul'a: “Davut aramızda gizleniyor” dedikleri zaman Ey Tanrı, beni adınla kurtar, Gücünle akla beni!
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Ey Tanrı, duamı dinle, Kulak ver ağzımdan çıkan sözlere.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
Çünkü küstahlar bana saldırıyor, Zorbalar canımı almak istiyor, Tanrı'ya aldırmıyorlar. (Sela)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
İşte Tanrı benim yardımcımdır, Tek desteğim Rab'dir.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
Düşmanlarım yaptıkları kötülüğün cezasını bulsun, Sadakatin uyarınca yok et onları.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
Ya RAB, sana gönülden bir kurban sunacağım, Adına şükredeceğim, çünkü adın iyidir.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
Beni bütün sıkıntılarımdan kurtardın, Gözlerim düşmanlarımın yok oluşunu gördü.

< Zabura 54 >