< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
För sångmästaren, med strängaspel; en sång av David, när sifiterna kommo och sade till Saul: "David håller sig nu gömd hos oss." Gud, fräls mig genom ditt namn, och skaffa mig rätt genom din makt.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Gud, hör min bön, lyssna till min muns tal.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
Ty främlingar resa sig upp mot mig, och våldsverkare stå efter mitt liv; de hava icke Gud för ögonen. (Sela)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
Se, Gud är min hjälpare, Herren uppehåller min själ.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
Må det onda falla tillbaka på mina förföljare, förgör dem, du som är trofast.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
Då skall jag offra åt dig med villigt hjärta; jag skall prisa ditt namn, o HERRE, ty det är gott.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
Ja, ur all nöd räddar det mig, och mitt öga får se med lust på mina fiender.

< Zabura 54 >