< Zabura 54 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
Reši me, oh Bog, po svojem imenu in sodi me s svojo močjo.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Usliši mojo molitev, oh Bog, pazljivo prisluhni besedam mojih ust.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
Kajti zoper mene so vstali tujci in zatiralci strežejo po moji duši; pred seboj si niso postavili Boga. (Sela)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
Glej, Bog je moj pomočnik. Gospod je s tistimi, ki podpirajo mojo dušo.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
Mojim sovražnikom bo povrnil zlo, odreži jih v svoji resnici.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
Velikodušno ti bom daroval, hvalil bom tvoje ime, oh Gospod, kajti to je dobro.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
Kajti osvobodil me je iz vseh težav in moje oko je videlo njegovo željo na mojih sovražnikih.