< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
Dem Vorsänger, mit Saitenspiel. Ein Maskil von David, als die Siphiter kamen und zu Saul sprachen: Hält David sich nicht bei uns verborgen? Gott, durch deinen Namen rette mich, und schaffe mir Recht durch deine Macht!
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Gott, höre mein Gebet, nimm du Ohren die Reden meines Mundes!
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
Denn Fremde sind wider mich aufgestanden, und Gewalttätige trachten nach meinem Leben; sie haben Gott nicht vor sich gestellt. (Sela)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
Siehe, Gott ist mein Helfer; der Herr ist unter denen, die meine Seele stützen.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
Er wird das Böse zurückerstatten meinen Feinden; nach deiner Wahrheit vertilge sie!
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
Opfern will ich dir mit Freiwilligkeit; deinen Namen will ich preisen, Jehova, denn er ist gut.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
Denn aus aller Bedrängnis hat er mich errettet; und mein Auge hat seine Lust gesehen an meinen Feinden.

< Zabura 54 >