< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
For the Chief Musician. On stringed instruments. A contemplation by David, when the Ziphites came and said to Saul, “Isn’t David hiding himself among us?” Save me, God, by your name. Vindicate me in your might.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Hear my prayer, God. Listen to the words of my mouth.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
For strangers have risen up against me. Violent men have sought after my soul. They haven’t set God before them. (Selah)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
Behold, God is my helper. The Lord is the one who sustains my soul.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
He will repay the evil to my enemies. Destroy them in your truth.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
With a free will offering, I will sacrifice to you. I will give thanks to your name, LORD, for it is good.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
For he has delivered me out of all trouble. My eye has seen triumph over my enemies.

< Zabura 54 >