< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
For the chief musician; on stringed instruments. A maschil of David; when the Ziphites came and said to Saul, “Does David not hide himself with us?” Save me, God, by your name, and judge me in your might.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
Hear my prayer, God; give ear to the words of my mouth.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
For strangers have risen up against me, and pitiless men have sought after my life; they have not set God before them. (Selah)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
See, God is my helper; the Lord is the one who upholds me.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
He will repay my enemies with evil; in your faithfulness, destroy them!
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
I will sacrifice to you with a freewill offering; I will give thanks to your name, Yahweh, for it is good.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
For he has rescued me from every trouble; my eye has looked in triumph on my enemies.

< Zabura 54 >