< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
God, by your power [MTY, DOU] save me [from my enemies], and show people that I have not done anything that is wrong!
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
God, listen to my prayer; listen to what I say to you,
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
because strangers are [trying to] attack me; proud men are wanting to kill me; men who do not have any (respect for/interest in) you.
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
But God is the one who helps me; Yahweh defends/protects me [from my enemies].
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
He will cause the evil things that they want to do to me to happen to them instead; because he faithfully [does what he promises], he will get rid of them.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
Yahweh, I will gladly give an offering to you because I want to, and I will thank you [MTY], for you are good [to me];
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
you have rescued me from all my troubles, and I have seen that you have defeated my enemies.

< Zabura 54 >