< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
“For the leader of the music. To be sung on stringed instruments A psalm of David, when the Ziphites came and said to Saul, Doth not David hide himself with us?” Save me, O God! by thy name, And by thy strength defend my cause!
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
O God! hear my prayer, Give ear to the words of my mouth!
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
For enemies have risen up against me, And oppressors seek my life; They have not set God before their eyes. (Pause)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
Behold! God is my helper; The Lord is the support of my life.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
He will repay evil to my enemies; For thy truth's sake, O God! cut them off!
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
With a willing heart will I sacrifice to thee; I will praise thy name, O LORD! for it is good;
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
For thou hast delivered me from all trouble, So that my eye hath looked with joy upon my enemies!

< Zabura 54 >