< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
For the end, among Hymns of instruction by David, when the Ziphites came and said to Saul, Behold, is not David hid with us? Save me, O God, by your name, and judge me by your might.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
O God, hear my prayer; listen to the words of my mouth.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
For strangers have risen up against me, and mighty men have sought my life: they have not set God before them. (Pause)
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
For behold! God assists me; and the Lord is the helper of my soul.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
He shall return evil to mine enemies; utterly destroy them in your truth.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
I will willingly sacrifice to you: I will give thanks to your name, O Lord; for [it is] good.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
For you have delivered me out of all affliction, and mine eye has seen [my desire] upon mine enemies.

< Zabura 54 >