< Zabura 54 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Zifawa suka tafi wurin Shawulu suka ce, “Ba Dawuda ba ne yake ɓuya a cikinmu?” Ka cece ni, ya Allah ta wurin sunanka; ka nuna ni marar laifi ne ta wurin ƙarfinka.
Unto the end. In verses, the understanding of David, when the Ziphites had arrived and they said to Saul, “Has not David been hidden with us?” Save me, O God, by your name, and judge me in your virtue.
2 Ka ji addu’ata, ya Allah; ka saurari maganar bakina.
O God, listen to my prayer. Pay attention to the words of my mouth.
3 Baƙi suna kawo mini hari; mutane marasa imani suna neman raina, mutanen da ba sa tsoron Allah. (Sela)
For strangers have risen up against me, and the strong have sought my soul. And they have not set God before their eyes.
4 Tabbatacce Allah ne mai taimakona, Ubangiji shi ne wanda yake riƙe ni.
For behold, God is my helper, and the Lord is the protector of my soul.
5 Bari mugunta ta shaƙe masu magana marar kyau a kaina; cikin amincinka ka hallaka su.
Turn back the evils upon my adversaries, and ruin them by your truth.
6 Zan miƙa hadaya ta yardar rai gare ka; zan yabe sunanka, ya Ubangiji, gama yana da kyau.
I will freely sacrifice to you, and I will confess your name, O God, because it is good.
7 Gama ya cece ni daga dukan wahalolina, idanuna kuma sun ga an yi nasara a kan maƙiyana.
For you have quickly rescued me from all tribulation, and my eye has looked down upon my enemies.

< Zabura 54 >