< Zabura 53 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat. Wani maskil na Dawuda. Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.
“For the leader of the music. To be sung on wind instruments. A psalm of David.” The fool saith in his heart, “There is no God!” They are corrupt; their doings are abominable; There is none that doeth good.
2 Allah yana duba daga sama a kan’ya’yan mutane yă ga ko akwai wani wanda ya gane, wani wanda yake neman Allah.
God looketh down from heaven upon the children of men, To see if there are any that have understanding, That have regard to God.
3 Kowa ya kauce, gaba ɗaya sun lalace; babu guda da yake aikata abu mai kyau, babu ko ɗaya.
They are all gone astray; together are they corrupt; There is none that doeth good, no, not one.
4 Masu aikata mugunta ba sa taɓa koyo? Suna cin mutanena kamar yadda ake cin burodi, ba sa kuma kira ga Allah.
Shall not the evil-doers be requited, Who eat up my people like bread, And call not upon God?
5 Ga shi fa, sun firgita don tsoro, ko da yake babu dalilin tsoro, gama Allah zai watsar da ƙasusuwan masu ƙinsa, za su sha kunya, gama Allah ya ƙi su.
Yea! fear shall come upon them, Where no fear is; For God will scatter the bones of him that encampeth against thee; Thou shalt put them to shame, for God despiseth them!
6 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Allah ya sāke arzuta mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
O that salvation for Israel would come out of Zion! When God bringeth back the captives of his people, Jacob shall rejoice, and Israel be glad.