< Zabura 53 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat. Wani maskil na Dawuda. Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.
“To the chief musician upon Machalath, a Maskil of David.” The worthless fool saith in his heart, There is no God. They are corrupt, and they are abominable [in their] injustice: there is none that doth good.
2 Allah yana duba daga sama a kan’ya’yan mutane yă ga ko akwai wani wanda ya gane, wani wanda yake neman Allah.
God looketh down from heaven upon the children of men, to see if there be one intelligent, one who seeketh for God.
3 Kowa ya kauce, gaba ɗaya sun lalace; babu guda da yake aikata abu mai kyau, babu ko ɗaya.
Every one [of them] hath departed [from righteousness]; altogether are they become corrupt: there is none that doth good, no, not one.
4 Masu aikata mugunta ba sa taɓa koyo? Suna cin mutanena kamar yadda ake cin burodi, ba sa kuma kira ga Allah.
Is there no knowledge in the workers of wickedness? who eat up my people as they eat bread: [while] they do not call on God.
5 Ga shi fa, sun firgita don tsoro, ko da yake babu dalilin tsoro, gama Allah zai watsar da ƙasusuwan masu ƙinsa, za su sha kunya, gama Allah ya ƙi su.
There were they terrified with terror where there was no terror; for God had scattered the bones of those that encamped against thee: thou didst put them to shame, because God had rejected them.
6 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Allah ya sāke arzuta mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
Oh that some one might bring the salvation of Israel out of Zion! When God bringeth back the captivity of his people, [then] will Jacob be glad, [and] Israel will rejoice.