< Zabura 52 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
Instrução de Davi, para o regente, quando Doegue, o edomita, veio, e contou a Saul, dizendo: Davi veio à casa de Aimeleque: Por que tu, homem poderoso, te orgulhas no mal? A bondade de Deus continua o dia todo.
2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
Tua língua planeja maldades; [é] como navalha afiada, que gera falsidades.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. (Sela)
Tu amas mais o mal que o bem, [e] a mentira mais do que falar justiça. (Selá)
4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Tu amas todas as palavras de destruição, ó língua enganadora.
5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. (Sela)
Porém Deus te derrubará para sempre; ele te tomará, e te arrancará para fora da tenda; e te eliminará de toda a terra dos viventes. (Selá)
6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,
E os justos [o] verão, e temerão; e rirão dele, [dizendo]:
7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”
Eis aqui o homem que não pôs sua força em Deus, mas [preferiu] confiar a abundância de suas riquezas, e fortaleceu em sua maldade.
8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.
Mas eu [serei] como a oliveira verde na casa de Deus; confio na bondade de Deus para todo o sempre.
9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.
Eu te louvarei para sempre, por causa do que fizeste; e terei esperança em teu nome, porque tu és bom perante teus santos.

< Zabura 52 >