< Zabura 52 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
Untuk pemimpin kor. Nyanyian pengajaran Daud, ketika Doeg, orang Edom, datang memberitahukan kepada Saul bahwa Daud sudah sampai di rumah Abimelekh. Hai orang kuat, mengapa engkau menyombongkan kejahatanmu terhadap orang yang dikasihi Allah?
2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
Sepanjang hari engkau menipu dan merencanakan yang jahat; lidahmu seperti pisau cukur yang tajam.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. (Sela)
Engkau lebih mencintai kejahatan daripada kebaikan, lebih suka berbohong daripada berkata benar.
4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Dengan kata-katamu engkau menipu dan menyakiti hati orang!
5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. (Sela)
Tetapi engkau akan dibinasakan Allah untuk selamanya; engkau ditangkap dan diseret dari rumahmu, dan dilenyapkan dari dunia orang hidup.
6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,
Melihat itu, orang saleh akan ketakutan, lalu menertawakan engkau dan berkata,
7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”
"Itulah orangnya yang tidak berlindung pada Allah, tetapi mengharapkan kekayaannya yang berlimpah dan mencari keamanan pada barang rampasannya."
8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.
Tetapi aku seperti pohon zaitun yang hijau di dalam Rumah Allah. Aku percaya bahwa Allah tetap mengasihi untuk selama-lamanya.
9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.
Aku selalu mau bersyukur kepada-Mu di depan umat-Mu kuwartakan kebaikan-Mu.