< Zabura 52 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
Maskil de David, donné au maître chantre. Sur ce que Doëg Iduméen vint à Saül, et lui rapporta, disant: David est venu en la maison d'Ahimélec. Pourquoi te vantes-tu du mal, vaillant homme? La gratuité du [Dieu] Fort dure tous les jours.
2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
Ta langue trame des méchancetés, elle est comme un rasoir affilé, qui trompe.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. (Sela)
Tu aimes plus le mal que le bien, [et] le mensonge plus que de dire la vérité; (Sélah)
4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Tu aimes tous les discours pernicieux, [et] le langage trompeur.
5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. (Sela)
Aussi le [Dieu] Fort te détruira pour jamais; il t'enlèvera et t'arrachera de [ta] tente, et il te déracinera de la terre des vivants; (Sélah)
6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,
Et les justes [le] verront, et craindront, et ils se riront d'un tel homme, [disant]:
7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”
Voilà cet homme qui ne tenait point Dieu pour sa force, mais qui s'assurait sur ses grandes richesses, et qui mettait sa force en sa malice.
8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.
Mais moi, je serai dans la maison de Dieu comme un olivier qui verdit. Je m'assure en la gratuité de Dieu pour toujours et à perpétuité.
9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.
Je te célébrerai à jamais de ce que tu auras fait ces choses; et je mettrai mon espérance en ton Nom, parce qu'il est bon envers tes bien-aimés.

< Zabura 52 >