< Zabura 52 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
Au chef de musique; pour instruire. De David; lorsque Doëg, l’Édomite, rapporta à Saül et lui dit: David est venu dans la maison d’Akhimélec. Pourquoi te glorifies-tu du mal, homme fort? La bonté de Dieu subsiste de jour en jour.
2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
Ta langue trame des malheurs, pratiquant la fausseté, comme un rasoir affilé.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. (Sela)
Tu as aimé le mal plus que le bien, le mensonge plus que la parole de justice. (Sélah)
4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Tu as aimé toutes les paroles de destruction, langue trompeuse!
5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. (Sela)
Aussi Dieu te détruira pour toujours; il te saisira et t’arrachera de ta tente, et il te déracinera de la terre des vivants. (Sélah)
6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,
Et les justes verront, et craindront, et ils se riront de lui:
7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”
Voilà l’homme qui n’a pas pris Dieu pour sa force, mais qui s’est confié en la multitude de ses richesses, et qui se fortifiait dans son avidité!
8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.
Mais moi, je suis dans la maison de Dieu comme un olivier vert. Je me confierai en la bonté de Dieu, pour toujours et à perpétuité.
9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.
Je te célébrerai à jamais, parce que tu l’as fait; et je m’attendrai à ton nom, car il est bon devant tes saints.