< Zabura 52 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Wani maskil ta Dawuda. Sa’ad da Doyeg mutumin Edom ya tafi wurin Shawulu ya ce masa, “Dawuda ya tafi gidan Ahimelek.” Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?
“To the chief musician, a Maskil of David, When Doeg the Edomite came and told Saul, and said unto him, David is come to the house of Achimelech.” What vauntest thou thyself of wickedness, O mighty man? the kindness of God endureth all the time.
2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.
Thy tongue deviseth mischiefs, like a sharpened razor, thou worker of deceit.
3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. (Sela)
Thou lovest evil more than good; falsehood more than speaking righteousness. (Selah)
4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!
Thou lovest all words of destruction, the tongue of deceit.
5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. (Sela)
[Therefore] God will also destroy thee for ever: he will take thee away, and pluck thee out of his tent, and root thee out of the land of life. (Selah)
6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,
And the righteous shall see it, and they will be afraid, and laugh concerning him:
7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”
“Lo, this is the man that made not God his fortress; but trusted in the abundance of his riches, relied proudly on his mischievous wickedness.”
8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.
But I am like a green olive-tree in the house of God: I trust in the kindness of God for ever and ever.
9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.
I will thank thee for ever, because thou hast done it: and I will wait on thy name, for [it is] good, before thy pious ones.

< Zabura 52 >