< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Davut Bat-Şeva'yla yattıktan sonra Peygamber Natan kendisine geldiği zaman Ey Tanrı, lütfet bana, Sevgin uğruna; Sil isyanlarımı, Sınırsız merhametin uğruna.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Tümüyle yıka beni suçumdan, Arıt beni günahımdan.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Çünkü biliyorum isyanlarımı, Günahım sürekli karşımda.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Sana karşı, yalnız sana karşı günah işledim, Senin gözünde kötü olanı yaptım. Bu nedenle, söylediklerinde haklı, Yargılarında adilsin.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Nitekim suç içinde doğdum ben, Günah içinde annem bana hamile kaldı.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Madem sen gönülde sadakat istiyorsun, Bilgelik öğret bana yüreğimin derinliklerinde.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Beni mercanköşkotuyla arıt, paklanayım, Yıka beni, kardan beyaz olayım.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Neşe, sevinç sesini duyur bana, Bayram etsin ezdiğin kemikler.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Bakma günahlarıma, Sil bütün suçlarımı.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Ey Tanrı, temiz bir yürek yarat, Yeniden kararlı bir ruh var et içimde.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Beni huzurundan atma, Kutsal Ruhun'u benden alma.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Geri ver bana sağladığın kurtuluş sevincini, Bana destek ol, istekli bir ruh ver.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Başkaldıranlara senin yollarını öğreteyim, Günahkârlar geri dönsün sana.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Kurtar beni kan dökme suçundan, Ey Tanrı, beni kurtaran Tanrı, Dilim senin kurtarışını ilahilerle övsün.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Ya Rab, aç dudaklarımı, Ağzım senin övgülerini duyursun.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Çünkü sen kurbandan hoşlanmazsın, Yoksa sunardım sana, Yakmalık sunudan hoşnut kalmazsın.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Senin kabul ettiğin kurban alçakgönüllü bir ruhtur, Alçakgönüllü ve pişman bir yüreği hor görmezsin, ey Tanrı.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Lütfet, Siyon'a iyilik yap, Yeruşalim'in surlarını onar.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
O zaman doğru sunulan kurbanlar, Yakmalık sunular, tümüyle yakmalık sunular, Seni hoşnut kılar; O zaman sunağında boğalar sunulur.

< Zabura 51 >