< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Ten misericordia de mí, o! Dios, conforme a tu misericordia; conforme a la multitud de tus miseraciones rae mis rebeliones.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Aumenta el lavarme de mi maldad; y límpiame de mi pecado.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Porque yo conozco mis rebeliones: y mi pecado está siempre delante de mí.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
A ti, a ti solo he pecado, y he hecho lo malo delante de tus ojos: porque te justifiques en tu palabra, y te purifiques en tu juicio.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
He aquí, en maldad he sido formado: y en pecado me calentó mi madre.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
He aquí, la verdad has amado en lo íntimo: y en lo secreto me hiciste saber sabiduría.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Purifícame con hisopo, y seré limpio: lávame, y seré emblanquecido más que la nieve.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Házme oír gozo y alegría: y harán alegrías los huesos que moliste.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Esconde tu rostro de mis pecados: y rae todas mis maldades.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Críame, o! Dios, un corazón limpio: y renueva un espíritu recto en medio de mí.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
No me eches de delante de ti: y no quites de mí tu Santo Espíritu.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Vuélveme el gozo de tu salud: y el Espíritu voluntario me sustentará.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Enseñaré a los prevaricadores tus caminos: y los pecadores se convertirán a ti.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Escápame de homicidios, o! Dios, Dios de mi salud: cante mi lengua tu justicia.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Señor, abre mis labios, y denuncie mi boca tu alabanza.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Porque no quieres sacrificio, que, si no, yo lo daría: holocausto no quieres.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Los sacrificios de Dios es el espíritu quebrantado: el corazón contrito y molido, o! Dios, no menospreciarás.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Haz bien con tu buena voluntad a Sión: edifica los muros de Jerusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Entonces te agradarán los sacrificios de justicia, el holocausto, y el quemado: entonces ofrecerán sobre tu altar becerros.

< Zabura 51 >