< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Al maestro de coro. Salmo de David. Cuando después que pecó con Betsabee, se llegó a él Natán. Ten compasión de mí, oh Dios, en la medida de tu misericordia; según la grandeza de tus bondades, borra mi iniquidad.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Lávame a fondo de mi culpa, límpiame de mi pecado.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Porque yo reconozco mi maldad, y tengo siempre delante mi delito.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
He pecado contra Ti, contra Ti solo, he obrado lo que es desagradable a tus ojos, de modo que se manifieste la justicia de tu juicio y tengas razón en condenarme.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Es que soy nacido en la iniquidad, y ya mi madre me concibió en pecado.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Mas he aquí que Tú te complaces en la sinceridad del corazón, y en lo íntimo del mío me haces conocer la sabiduría.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Rocíame con hisopo, y seré limpio; lávame Tú, y quedaré más blanco que la nieve.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Hazme oír tu palabra de gozo y de alegría, y saltarán de felicidad estos huesos que has quebrantado.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Aparta tu rostro, de mis pecados, y borra todas mis culpas.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Crea en mí, oh Dios, un corazón sencillo, y renueva en mi interior un espíritu recto.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
No me rechaces de tu presencia, y no me quites el espíritu de tu santidad.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Devuélveme la alegría de tu salud; confírmame en un espíritu de príncipe.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Enseñaré a los malos tus caminos; y los pecadores se convertirán a Ti.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Líbrame de la sangre, oh Dios, Dios Salvador mío, y vibre mi lengua de exultación por tu justicia.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Abre Tú mis labios, oh Señor, y mi boca publicará tus alabanzas,
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
pues los sacrificios no te agradan, y si te ofreciera un holocausto no lo aceptarías.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Mi sacrificio, oh Dios, es el espíritu compungido; Tú no despreciarás, Señor, un corazón contrito [y humillado].
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Por tu misericordia, Señor, obra benignamente con Sión; reconstruye los muros de Jerusalén.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Entonces te agradarán los sacrificios legales, [las oblaciones y los holocaustos]; entonces se ofrecerán becerros sobre tu altar.

< Zabura 51 >