< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Salmo de Davi, para o regente, quando o profeta Natã veio até ele, depois dele ter praticado adultério com Bate-Seba: Tem misericórdia de mim, ó Deus, conforme a tua bondade; desfaz minhas transgressões conforme a abundância de tuas misericórdias.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Lava-me bem de minha perversidade, e purifica-me de meu pecado.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Porque eu reconheço minhas transgressões, e meu pecado está continuamente diante de mim.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Contra ti, somente contra ti pequei, e fiz o mal segundo teus olhos; para que estejas justo no que dizeres, e puro no que julgares.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Eis que em perversidade fui formado, e em pecado minha mãe me concebeu.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Eis que tu te agradas da verdade interior, e no oculto tu me fazes conhecer sabedoria.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Limpa-me do pecado com hissopo, e ficarei limpo; lava-me, e eu serei mais branco que a neve.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Faça-me ouvir alegria e contentamento, [e] meus ossos, que tu quebraste, se alegrarão.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Esconde tua face de meus pecados, e desfaz todas as minhas perversidades.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Cria em mim um coração puro, ó Deus; e renova um espírito firme em meu interior.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Não me rejeites de tua face, e não tires teu Espírito Santo de mim.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Restaura a alegria de tua salvação, e que tu me sustentes com um espírito de boa vontade.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
[Então] eu ensinarei aos transgressores os teus caminhos, e os pecadores se converterão a ti.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Livra-me das [transgressões] por derramamento de sangue, ó Deus, Deus de minha salvação; e minha língua louvará alegremente tua justiça.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Abre, Senhor, os meus lábios, e minha boca anunciará louvor a ti.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Porque tu não te agradas de sacrifícios, pois senão eu te daria; tu não te alegras de holocaustos.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Os sacrifícios a Deus são um espírito quebrado [em arrependimento]; tu não desprezarás um coração quebrado e triste.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Faze bem a Sião conforme tua boa vontade; edifica os muros de Jerusalém.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Então tu te agradarás dos sacrifícios de justiça, dos holocaustos, e das ofertas queimadas; então oferecerão bezerros sobre teu altar.

< Zabura 51 >