< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
Dāvida dziesma. Dziedātāju vadonim. Kad pravietis Nātans pie viņa nāca, kad viņš bija gājis pie Batsebas. Apžēlojies par mani, ak Dievs, pēc Savas žēlastības, izdeldē manus pārkāpumus pēc Savas lielās sirdsžēlastības!
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Mazgā mani labi no manas noziedzības un šķīstī mani no maniem grēkiem.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Jo es atzīstu savus pārkāpumus, un mani grēki ir manā priekšā vienmēr.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Tev vienam es esmu grēkojis un ļaunu darījis priekš Tavām acīm, ka Tu palieci taisns Savos vārdos un šķīsts Savā tiesā.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Redzi, noziedzībā esmu dzemdināts, un grēkos māte mani ieņēmusi.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Redzi, tev patīk sirds patiesība, tad dari man zināmu to apslēpto gudrību.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Šķīstī mani no grēkiem ar īzapu, ka topu šķīsts, mazgā mani, ka topu baltāks nekā sniegs.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Liec man dzirdēt prieku un līksmību, ka tie kauli līksmojās, ko Tu esi satriecis.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Apslēp Savu vaigu no maniem grēkiem un deldē visu manu noziegumu.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Radi iekš manis, ak Dievs, šķīstu sirdi un atjauno iekš manis pastāvīgu garu.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Nemet mani nost no Sava vaiga, un neatņem no manis Savu Svēto Garu.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Atdod man atkal Savas pestīšanas prieku, un uzturi mani ar labprātīgu garu.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Tad es mācīšu pārkāpējiem Tavus ceļus, ka grēcinieki pie Tevis atgriežas.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Izglābi mani no asins vainām, ak Dievs, tu Dievs mans Pestītājs; tad mana mēle slavēs Tavu taisnību.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Kungs, atdari manas lūpas, tad mana mute izteiks Tavu slavu.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Jo Tev netīk upuris, citādi es to gribētu dot, dedzināms upuris Tev nepatīk.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Dieva upuris ir satriekts gars; salauztu un sagrauztu sirdi Tu, Dievs, nesmādēsi.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Dari labu Ciānai pēc Savas labprātības, uztaisi Jeruzālemes mūrus.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Tad Tev patiks taisnības upuri, dedzināmais un visa(kopējais) sadedzināmais upuris, tad upurēs vēršus uz Tava altāra.

< Zabura 51 >