< Zabura 51 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
In finem, Psalmus David, Cum venit ad eum Nathan Propheta, quando intravit ad Bethsabee. Miserere mei Deus, secundum magnam misericordiam tuam. Et secundum multitudinem miserationum tuarum, dele iniquitatem meam.
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Amplius lava me ab iniquitate mea: et a peccato meo munda me.
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Quoniam iniquitatem meam ego cognosco: et peccatum meum contra me est semper.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Tibi soli peccavi, et malum coram te feci: ut iustificeris in sermonibus tuis, et vincas cum iudicaris.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Ecce enim in iniquitatibus conceptus sum: et in peccatis concepit me mater mea.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Ecce enim veritatem dilexisti: incerta, et occulta sapientiæ tuæ manifestasti mihi.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Asperges me hyssopo, et mundabor: lavabis me, et super nivem dealbabor.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Auditui meo dabis gaudium et lætitiam: et exultabunt ossa humiliata.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Averte faciem tuam a peccatis meis: et omnes iniquitates meas dele.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Cor mundum crea in me Deus: et spiritum rectum innova in visceribus meis.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Ne proiicias me a facie tua: et Spiritum Sanctum tuum ne auferas a me.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Redde mihi lætitiam salutaris tui: et spiritu principali confirma me.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Docebo iniquos vias tuas: et impii ad te convertentur.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Libera me de sanguinibus Deus, Deus salutis meæ: et exultabit lingua mea iustitiam tuam.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Domine, labia mea aperies: et os meum annunciabit laudem tuam.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Quoniam si voluisses sacrificium, dedissem utique: holocaustis non delectaberis.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
Sacrificium Deo spiritus contribulatus: cor contritum, et humiliatum Deus non despicies.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
Benigne fac Domine in bona voluntate tua Sion: ut ædificentur muri Ierusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Tunc acceptabis sacrificium iustitiæ, oblationes, et holocausta: tunc imponent super altare tuum vitulos.

< Zabura 51 >