< Zabura 51 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
[Psalm lal David, Tukun Mwet Palu Nathan el Kaskas nu sel ke Tafongla lal yorol Bathsheba] Pakoten nu sik, O God, Ke sripen lungse kawil lom! Ke pakoten lulap lom, Eela ma koluk luk!
2 Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
Ohlla ma koluk luk nukewa Ac aknasnasyeyula liki ma koluk luk!
3 Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
Nga akilen tafongla luk, Ac ma koluk luk oan in nunak luk pacl e nukewa.
4 Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
Nga oru ma koluk lain kom, aok lain kom mukena, Ac oru ma su tia wo ye motom. Ke ma inge fal kom in nununkeyu. Oasr suwohs lom in lisyula.
5 Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
Nga nuna koluk oe ke len se nga isusla ah me; Liki pacl se nga srimetak, nga nuna mwet koluk.
6 Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
Orekma suwohs ac inse pwaye pa kom lungsum; Nwakla nunak luk ke lalmwetmet lom.
7 Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
Aknasnasyeyu ke sak hyssop, ac nga fah nasnasla; Oulyula ac nga fah fasrfasr liki snow.
8 Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
Lela nga in lohng pusren engan ac insewowo; Finne kom tuh itungyuwi ac kunausyula, Nga ac sifil pacna enganak.
9 Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
Afinya motom liki ma koluk luk Ac eela ma koluk luk nukewa.
10 Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
Kom in oru insiuk in nasnas, O God, Ac ase sie ngun sasu ac pwaye in nga.
11 Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
Nikmet lisyula liki ye motom; Nikmet eisla ngun mutal lom likiyu.
12 Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
Sifilpa ase nu sik engan su tuku ke molela lom, Ac oru tuh nga in insewowo in akos kom.
13 Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
Na nga fah luti mwet koluk ke ma kom sapkin, Ac elos ac fah foloko nu yurum.
14 Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
Sruokya moul luk, O God, ac moliyula, Ac nga fah engan in fahkak ke suwoswos lom.
15 Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
Leum, kasreyu tuh nga in ku in kaskas, Ac nga fah kaksakin kom.
16 Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
Kom tia lungse mwe kisa; Kom funu lungse, nga lukun orek kisa; Kom tiana insewowo ke mwe kisa firir.
17 Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
O God, mwe kisa luk uh pa inse pusisel — Kom ac tia pilesru sie inse pusisel su auliyak.
18 Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
O God, kulang nu sin Zion ac kasrel; Sifilpa musaeak pot Jerusalem.
19 Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.
Na kom fah insewowo ke mwe kisa pwaye Ac ke mwe kisa firir lasr; Ac cow mukul fah kisakinyuk fin loang lom.